Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Afrika tayi bankwana da cutar polio – WHO

Published

on

Hukumar lafiya ta duniya WHO ta ayyana nahiyar Afurka a matsayin yankin da yayi bankwana da cutar shan inna wato Polio.

A cewar hukumar ta WHO rabuwar nahiyar da cutar ta polio tun a shekarar dubu biyu da goma sha shida.

Hukumar lafiya ta duniyar ta ce, kawo karshen cutar daya ne daga cikin bajinta da aka taba gani a bangaren lafiya a tarihin duniya.

Hakan na cikin wata sanarwa ce da hukumar ta WHO ta fitar a yau talata mai dauke da sa hannun shubagan hukumar, Dr Tedros Adhanom Ghebreyesus da kuma shugaban kungiyar Rotary International, Holger Knaack.

Sanarwar ta kuma jinjinawa kokarin da ta ce nahiyar afurka ta yi da kuma dukkannin wadanda suka ba da gudunmawa wajen ganin an dakile cutar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!