Connect with us

Labarai

Za a samu ɗaukewar ruwan famfo a wasu sassan birnin Kano

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da cewa akwai yiwuwar za a samu ɗaukewar ruwan famfo a wasu sassan birnin Kano sakamakon gyare-gyaren da ake yi kan layin wutar lantarki da ke samar wa Matatar Ruwa ta Challawa wuta.

Wannan na cikin sanarwar da Kwamishinan Albarkatun Ruwa, na Jihar Kano, Dr. Dahir M. Hashim, ya fitar.

Sanarwar ta bayyana cewa Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na KEDCO na gudanar da gyaran layin wutar Challawa, yayin da kuma ake gyaran injinan wutar da ake amfani da su a matatar ruwan.

Gwamnatin ta ce za a dawo da samar da ruwan famfo yadda aka saba da zarar an maido da wutar lantarki da kuma kammala gyare-gyaren da ake yi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!