Connect with us

Labarai

Al’ummar Kano su girmama dokar hana fita-Women rights

Published

on

Wata kungiya  dake rajin kare hakkin dan Adam ta kasa da kasa wato youth for women rights international ta yi Kira ga al’ummar jihar Kano dasu girmama dokar da mahukunta suka zartar na zaman gida tsahon mako guda.

Shugaban kungiyar Nuraddeen Sani Abbdullahi ne yayi kiran a wata tattaunawa da Freedom Radiyo a daren jiya alhamis.

Ya kara da kiran jami’an tsaro dasuyi aiki bisa yadda doka ta basu dama ba tare da samun zargin sun cin zarafin mutane ba.

Nuradden Sani ya yabawa Malamai da ma’aikatan lafiya da kuma ‘ yan jaridu bisa yadda suke aiki tukuru domin kawar da Covid-19 daga jihar Kano.

kungiyar ta kuma yi kira ga masu hali da su taimakawa marasa karfin dake kusa dasu.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!