Connect with us

Labarai

Ambaliyar ruwa ta jefa dubban mazauna Jihar Yobe cikin mawuyacin hali

Published

on

Ambaliyar ruwa da guguwa mai ƙarfi sun jefa dubban mazauna Jihar Yobe cikin mawuyacin hali, inda mutane 34,533 daga iyalai 9,845 suka fuskanci matsalar a ƙananan hukumomi 15 na jihar.

 

Hukumar ba da agajin gaggawa ta Jihar Yobe, YOSEMA, ta ce mutane 11 sun rasa rayukansu, yayin da wasu 303 suka samu raunuka tun daga ranar 8 ga watan Mayu zuwa 10 ga watan Agustan 2026.

 

Rahoton hukumar ya kuma bayyana cewa gidaje da ɗakuna sama da 21,000 sun lalace ko kuma suka ruguje, lamarin da ya tilasta wa mutane 1,120 barin gidajensu domin neman mafaka.

 

Karamar hukumar Karasuwa ce ta fi fama da iftila’in, inda mutane dubu 3,288 abin ya shafa.

 

A babban birnin jihar Damaturu ambaliyar ta shafi mutane 1,554 tare da haddasa mutuwar mutum guda.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!