Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Jigawa

Ambaliyar ruwa : Mutane 23 sun rasa rayuka a jihar Jigawa

Published

on

Kimanin mutane 23 ne suka mutu a sanadiyar ambaliyar ruwa da ta faru a kananan hukumomin jihar Jigawa 24 da sauyawa iyalai sama da dubu hamsin matsugunan su.

Shugaban hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Yusuf Babura ne ya tababtar da hakan, inda ya ce galibin wadanda suka rasun kananan yara ne.

Babura na cewa rushewar gine-gine sanadiyar mamakon ruwan sama na daga cikin dalilan da suka sabbaba mutuwar mutanen.

Rahotanni na nuni da cewa, an samu mutuwar mutane hudu a Gwaram da uku a Babura da Ringim da Malam Madori da kuma wasu biyu a Birnin Kudu da Guri.

Shugaban hukumar ya kara da cewa ambaliyar ruwan ta shafi kananan hukumomi 24 cikin 27 na jihar ta Jigawa, banda kananan hukumomi 17 da lamarin ya fi yin kamari.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!