Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Yawan amfani da bayanai ga ma’aikatu zai kawo cigaba a Nijeriya- CITAD

Published

on

Cibiyar bunkasa fasahar sadarwa da ci gaban al’umma a Kano CITAD, ta bukaci gwamnatin tarraya da ta kara zaburar da ma’aikatu da hukumomin kasar nan da su ringa amfani da bayanai akai-akai wajen gudanar da ayyukansu da ciyar da su gaba.

Shugaban cibiyar Alhaji Zakari Yau ne ya bayyana hakan a taron manema labarai wadda ya gudanar jiya a nan Kano.

A cewarsa, ‘bayanai na taka muhimmiyar rawa wajen gudanar ayyuka musamman a zamanance’.

Ya kuma ce, ‘a wani rahoto da cibiyar gudanar ayyuka ta duniya ta fitar ya nuna cewa, kasashen Afirka da dama ciki kuwa har da Nijeriya na fama da matsalar rashin amfani da bayanai yadda ya kamata wajen gudanar da aiki’.

Freedom Radio ta ruwaito cewa, cibiyar ta kuma ja hankulan gwamnatoci a dukkannin matakai da su kasance masu kiyaye bayanai duba da muhimmancinsu.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!