Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Amsoshin tambayoyi 20 kan cutar Corona – Dr. Ibrahim Musa

Published

on

Wadannan wasu ne daga amsoshin tambayoyin ku da likitan mu Dakta Ibrahim Musa na asibitin koyawarwa na Malam Aminu Kano ya amsa muku ta shafin mu na Facebook wato Freedom Radio Nigeria.

  1. Tambaya ta farko:

Sani Mai Rodi

Wai Dan Allah Mai yasa ba a Nuna Mana masu cutar Coronavirus a fili Dan Al’umma su kara tabbatar da akwai ciwon.

Ibrahim Musa
Akwai confidentiality na marar lafiya.

Mus’ab Ibrahim Sulaiman

Amma Mai Coronar Nigeria kadai keda confidentiality ko, tunda muna ganin na sauran kasashe

Ibrahim Musa

Idan mara lafiya ya bada izni ‘yan jaridu za su iya daukar hotonsa.

Wannan aikin yan jaridu ne bana hukumar lafiya ba, Wanda ya fara kamuwa da ita a Kano anyi ta yamididi da sunansa ana bata shi.

Wannan yasa saboda kiyaye hakkinsu ba a fada sai ga wanda ya zama a hakku.

 

  1. Tambaya ta biyu:

Sagir Umar Sheka

Ina muku fatan alkhairi tambayata ita ce zuwa yaushe suke sa ran zasu shawo kan wannan cutar corona

Ibrahim Musa 
Anci karfin ciwon sosai, Insha Allah nan bada dadewa ba za’a shawo kan ciwon.

 

  1. Tambaya ta uku:

Muhammad S Muhammad

Aslm Dakta Wanda yake da Covid-19 Bayan mutum ya kamu da ita idan ya warke ya rabu da ita baki daya ne ko kuma akwai wasu illoli da take yiwa mutum a jiki?.

Ibrahim Musa
Tunda sabon ciwo ne, ba za a iya sanin ko akwai wasu matsaloli ba sai nan gaba. Wadansu sukan samu stroke saboda ciwon wanda ko mutum ya warke zai fama dashi zuwa wani lokaci.

 

  1. Tambaya ta hudu:

Abdulganiyu Isah Wagini

Aslm Dakta tambayata anan ita ce,
Ta wanne irin hanyoyi zakayi mu’amala da wanda ya kamu da korona kuma ya warke, sannan kuma wacce hanya al’umma zasu bi domin dakile cutar nan ba tare da ta ci gaba da yaduwa ba a cikin al’umma, Nagode a tashi lafiya.

Ibrahim Musa 
Idan ya warke sai a cigaba da mu’amala babu matsala.

Amma a kula da tsaftar hannu, tsaftar jiki da tsaftar muhalli.

A rika bada tazara ta taku shida idan an shiga taro.

A saka Facemask duk lokacin da ake waje.

Banda musabiha ko saka hannu ana dakuma fuska.

Idan mutum yaji bashi da lafiya, ya killace kansa har sai an gano mai ke damunsa anyi masa magani ya warke, Shine za a iya dakile yaduwar ciwon.

 

  1. Tambaya ta biyar:

AbdulJabbar Musa 

Salam Dakta Tambayata itace: “ko akwai wata na’ura da jami’an lafiya zasu yi amfani da ita wajen gwajin kwayar cutar CORONA wadda zata nuna sakamakon nan take kamar yadda Infrared Thermometer take nunawa?.
Sannan kuma meyasa jami’an tsaro na bakin border ba’a basu kayan aiki (personal protective equipment) kamar yadda na lafiya suke samu?”

Ibrahim Musa

Akwai na’urar dake nuna ciwon cikin minti 15, amma ba a Nigeria ba.

Ba mamaki nan gaba a kawo ta tunda bata dade da fitowa ba.

PPE suna ne mai fadi, Maaikatan border idan suka saka facemask da gloves sun isa.

A asibitin ma su ake sawa sai kalilan dake duba masu COVID-19 dake saka full protective gear. Ita full gear tana da zafi wanda a awa daya mutum na iya gumi da yakai litre guda.

 

  1. Tambaya ta shida:

Murtala Yahaya Musa Sarauta 

Assalamu alaikum,
Muryar jama a Allah ya taimakeku.
Tambayata Itace Idan na kasa samun lambar masu zuwa sudauki wanda yake da alamomin wannan cutar me yakamata nayi domin dakile cutar da kuma ni na samu sauki kafin Allah yasa na same su a waya.

Ibrahim Musa
Killace kai. Cin abinci mai gina jiki. Shan ruwa sosai. Tsaftar hannu da ta jiki. Yawan shan kayan marmari da yayan itatuwa.

Idan kaji kamar ciwon zai galabaitar da kai kaje asibiti ka sanar dasu halin da kake ciki.

 

  1. Tambaya ta bakwai:

Ilyasu Bin Galadimawa 

Slm fatan alkhairi a gareku ina yiwa babban bako barka da zuwa tambaya ta itace ta yaya mutun zai san ya kamu da wannan cutar sannan kuma ta yaya zai sanar daku Allah ya maida bako gida lfy.

Ibrahim Musa 
Alamomin ciwon sun hada da zazzabi, tari mara kaki, shakewa ko daukewar numfashi, gudawa, ciwon jiki, rashin jin kamshi ko dandano. Idan kana jin daya ko duka alamomin sai ka kira lambar State Rapid Response ta jiharka suzo suyi maka gwaji a tabbatar ko kana da ciwon.

 

  1. Tambaya ta takwas:

Baban Humaira Rimin Kebe

Tambaya ta anan shine don Allah Freedom ance a zauna a gida amma har yanzu kullum ana samun karin mutane a nan jihar Kano to yanzu haka za a yi ta tafiya?

Ibrahim Musa 
Zaman gida yana rage yaduwar ciwon ne amma tunda ba kowa ne ke zaman gidan ba har yanzu ana samun mutane suna hada-hada da cakuduwa.

Wannan yasa ciwon yake cigaba amma ba kamar yadda da an bar kowa yayi abinda ya ga dama ba.

 

  1. Tambaya ta tara:

Sulaiman Gambo Idris

SLM ya maganar maganin da aka karbo daga Madagascar yaushe za a fara amfani dashi a nan Nigeria kuma ina kira da likitoncin mu suma yakamata suyi hobbasa su samar da maganin wannan cuta.

Ibrahim Musa 
Maganin Madagascar na gargajiya ne. Shugaban kasa yace ayi bincike a tabbatar da menene shi tukun kafin ya a cewa jama’a suyi amfani dashi.
Likitocin Nigeria suna iya kokarin su. Bincike irin wannan yana bukatar kudi da kayan gwaje-gwaje.

 

  1. Tambaya ta goma:

Jameelah T Rabiu

Tambayoyi na Dakta su ne, Wanda ya kamu ya warke yana iya kuma kamuwa? a wani qaulin ance bata kama yara, ya abin yake? idan mutum yaji alamu a jikinsa ba tare da an gwadashi ba, me ya kamata yayi?

Ibrahim Musa 

Tambaya ta daya na amsa ta a sama. Ta biyu amsar itace tana kama yara sai dai bata cika tsanani a jikinsu ba.

Idan mutum yaji alamun corona sai ya killace kansa, ya kuma kira ayi masa gwaji.

 

  1. Tambaya ta goma sha daya:

Abubakar Fulani Goron Dutse 

Slm, ya aiki Allah ya taimaka yayi jagora, shin wai dagaske ne ace coronavirus ta kusa yin experience, kuma da gaske ke Nigeria tana daga cikin kasashen da suka Nemo maganin ta?

Ibrahim Musa 
Kana nufin expiry? Har yanzu dai ana fama da ciwon. Amma abubuwa na dada lafawa a hankali.

Nigeria tana nata kokarin. Amma har yanzu dai ba’a samu wani magani Dan Nigeria ba.

 

  1. Tambaya ta goma sha biyu:

Auwal Shuaibu Amfani

Fatan alkhairi ga wannan tasha mai farin jini kuma ina yiwa masu gabatar da wannan shirin barka da shigowa studio, tambayata ita ce mai cutar covid-19 zai iya warkewa daga cutar gaba daya kuma cutar ta kara kamashi a karo na biyu 2.

Ibrahim Musa 

An samu wasu gwaji ya nuna sun kamu da Corona bayan warkewa.

Amma daga baya anyi tunanin ko ragowar matattun RNA na virus dinne ba wai sabon ciwo bane.

 

  1. Tambaya ta goma sha uku:

Uban Salo 
Tambayata ita ce wai shin coronavirus a ina ake killace al’umma wadanda suka kamu da ita, kuma sai naga ban taba jin wanda akace min gashi wani dan uwansa ya kamu da ita menene sirrin lamarin ne?

Ibrahim Musa

Ana killace wadanda suka kamu da ita ne a asibitocin da gwamnati da ware da sunan isolation centers.

A Kano sun hada da asibitin Kwanar Dawaki da kuma Muhammad Buhari Specialists Hospital dake Giginyu.
Mutane da yawa ‘yan uwansu ko iyayensu ko abokansu sun kamu da ita. Wasu ma ita ta jawo ajalinsu. Ba mamaki baka taba ganin wanda ya kamu HIV ba. Amma hakan baya nufin babu HIV.

 

  1. Tambaya ta goma sha hudu:

Aremeenu Ubalee Gaya 

Assalamu alaikum ina yiwa babban likita barka da zuwa tambayata itace ance har yanzu ba’a kai ga gano maganin corona virus ba amma kuwa munji ana warke to wai tayaya ake warkewa daga wannan cuta.

Ibrahim Musa
Da yawa garkuwar jikin Dan Adam ce take yakar cutar. Wadansu da ake kwantarwa ana basu kulawa da tallafi har sai garkuwar jikinsu tayi tasiri ta murkushe ciwon.

 

  1. Tambaya ta sha biyar:

Aminu Abubakar 

Assalamu alaikum kowa ya yarda akwai corona amma abun tambaya shine me yasa ba a nuna mana marasa lafiyar?, me yasa bama ganin video lokacin da ake basu kulawa me yasa bamu taba ganin wanda yace an dauki dan uwansa ko dan unguwarsu mai cutar ba?, saidai kullum muji cewa an samu mutun kaza bamu gamsuba, bamu san su ba, kuma muna da abokai a kowace unguwa acikin garin nan.

Ibrahim Musa
Saboda mara lafiya nada sirri da bai kamata a tozarta shi ba sai dai idan shi ne da kansa ya fadawa alumma.

 

  1. Tambaya ta sha shida:

Usman Mukhtar Muhammad 
Tambayata a nan shine wai wani irin magani kasar China tayi amfani dashi da ta samu lagon cutar covid-19 sosai?.

Ibrahim Musa

Babban maganin da tayi amafani dashi shine yin gwaji, killace wadanda ke da ciwon domin basu kulawa ta musamman, da kuma zakulo wadanda mai ciwon yayi mu’amala dasu a gwada su a gano suwa suka kamu.

Sannan kasar ta kulle garin Wuhan har sai da aka ga Corona ta daina yaduwa a tsakanin alumma.

 

  1. Tambaya ta sha bakwai:

Abbakar Sadeeq Abbakar 

Slm ina yiwa babban bako barka da zuwa tambayata a nan guda daya ce, wai shin wadanda ake samu da corona mai yasa ba a fadar sunan su da kuma local govenment dinsu?.

Ibrahim Musa
Saboda kowanne mara lafiya yana da ‘yancin a sirrinta abinda ya shafe shi. Ana kiran abin da confidentiality.

 

  1. Tambaya ta sha takwas:

Yusif Abban Anisah Karwai 

Slm zan iya kamuwa da corona idan nayi amfani da dardumar wanda yake dauke da ita?

Ibrahim Musa
Yana iya yiwuwa amma bashi ne hanyar da tafi yaduwa ba.

 

  1. Tambaya ta sha tara:
    Usman Lawal

Wai wadanda ake samu sun warke daga cutar wane irin magani ne suke sha domin mu tanada.

Ibrahim Musa
Ana basu tallafi kalakala. Kowanne magani sai likita yaga dacewar sa kafin ya bayar.

 

  1. Tambaya ta ashirin:

Abdulkabeer Muhammad Jamiu

Ina da tambayoyi guda biyu kamar haka:

(1) shin sauro zai iya yada cutar korona?

(2) Jariri da mai dauke da cutar corona ta haifa, shin zai iya daukar cutar?

Ibrahim Musa 

Sauro baya yadata. Akwai yiwuwar jariri ya iya dauka.

Amma yawancin yara basa samun ciwo mai tsanani.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!