Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

An ƙaddamar da shirin ƙidayar yara da mata

Published

on

Hukumar kididdiga ta jihar Kano ta kaddamar da shirin samar da bayanai na yara ‘yan kasa da shekaru 5 da mata dake tsakanin shekarun haihuwa.

Shugaban hukumar Malam Baballe Ammani, ne ya shaida hakan, yayin kaddamar da shirin na MIC 6.

Yace shirin wanda hadaka ne da sauran Kungiyoyin tallafi na duniya, zai maida hankali ne wajen kula da bayanan walwalar mata da sauran bukatun su, tare da kananan yara dake samun rigakafin cututtuka.

Da take jawabi tun da fari, shugabar shirin na MICS/NICS Abiola Arosanye, ta bayyana cewa shirin zai kwashe tsawon watanni uku ana gudanar da shi.

Ta kara da cewa shirin zai maida hankali wajen samar da bayanan al’umma da matsalolin da suke fuskanta ga Gwamnati, don daukar matakan da suka kamata.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!