Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

An fara binciken wadanda suke da hannu a asarar hannayen jari da Najeriya ta yi

Published

on

Gwamnatin tarayya ta fara gudanar da tambayoyi ga mutanen da ake zargi suna da hannu cikin wata badakala wanda ta yi sanadiyar al’ummar kasar nan dubu sittin da biyar su ka yi asarar hannayen jari da suka zuba cikin wani kamfani da ya kai dala biliyan biyu

 

Wadana aka gayyata Kason farko don yi musu tambayoyi sun hada da: tsohon Ministan kasafin kudi da tsare-tsare Sanata Udoma Udo Udoma da takwaransa na kasuwanci da zuba jari Okechukwu Enelamah.

 

Lauyan wadanda suka fallasa badakalar da ya janyo asarar Chukwuemeka Obasi shi ya bayyana haka ga manema labarai jiya a Abuja.

 

A cewar sa jami’an tsaro sun kuma yi tambayoyi ga manajan daraktan bankin Union Emeka Emuwa wand shi ana zargin yana da hannu wajen faruwar lamarin.

 

Mr Chukwuemeka Obasi ya kuma ce duk wani kamfani ma zaman kansa da hukumomi da cibiyoyin gwamnati da ke da hannu cikin lamarin tuni sun gurfana don amsa tambayoyi

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!