Labarai
An bayyana kasashen da Nijeriya za ta kara da su a gasar matasa ‘yan kasa da shekaru 23.
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2019/10/U23-AFCON-draw-2019.png)
Kungiyar kwallon kafa ta Najeriya ta matasa ‘yan kasa da shekaru 23 za ta kara da kasar Afrika ta kudu da Zambia da Cote d’Ivoire a rukunin B a gasar cin kofin Afrika ta matasa ‘yan kasa da shekaru 23 na shekarar bana.
Mai masukin baki kasar Masar ta fada a rukunin A wanda ke kunshe da kasashen Ghana da Cameroon da kuma kasar Mali.
A jiya Laraba ne aka fitar da rukunan gasar a birinin Alexandria dake kasar Masar wadda zata gudana daga ranar 9 ga watan nuwamba zuwa ranar 22 ga watan na nuwamba.
Za fafata wasannin ne a filayen wasa guda 2, wato babban filin wasa na Cairo da filin wasa na Al Salam Stadium
Nigeria dai ita ce mai rike da kambun gasar bayan da ta lashe a shekarar a 2015.
Kungiyoyi uku da suka samu nasara a gasar sune zasu wakilci nahiyar Afrika a gasar gasar cin kofin duniya ta matasa ‘yan kasa da shekaru 23 wadda zata gudana a birnin Tokyo na kasar Japan a shekarar 2020.