Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

An dakatar da jirgin saman Emirates fita daga Najeriya – NCAA

Published

on

Gwamnatin tarayya ta dakatar da kamfanin jirgin sama na Emirates daga fita Najeriya tsawon sa’o’i 72.

 

Hukumar kula da sufurin Jiragen sama ta Najeriya ce ta sanar da hukuncin.

 

Dakatarwar dai ta biyo bayan sabawa ka’idojin da kwamitin kar ta kwana mai yaki da cutar corona na shugaban kasa ta sanya don yaki da cutar.

 

Ana zargin kamfanin jirgin da dauko fasinjoji ba tare da yin gwajin cutar corona ba, a don haka hukumar ta dakatar da tashin jiragen daga filayen jirgin saman Murtala Mohammed da ke Lagos da kuma na Nnamdi Azikwe da ke Abuja.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!