Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

An dakatar da kasar Mali daga kungiyar ECOWAS

Published

on

Kungiyar bunkasa tattalin arzikin kasashen yammacin Afurka ta ECOWAS ta dakatar da kasar Mali daga ci gaba da kasancewa mamba a cikin kungiyar.

Ecowas ta ce ta dau wannan mataki ne a matsayin mai da martini ga juyin mulki da sojoji su ka yi ga shugaba Ibrahim Boubacar Keita

Bugu da kari kungiyar ta ECOWAS ta kuma sha alwashin sanya takunkumin karya tattalin arziki ga kasar.

A jiya talata ne dai sojoji a kasar ta Mali suka kama Ibrahim Boubacar Keita da firaministan kasar, Boubou Cisse tare da tursasa shi yin murabus.

A cikin wata sanarwa da kungiyar ta ECOWAS ta fitar a yau Talata, ta ce, za ta dauki matakin rufe kan iyakokin kasashe mambobin kungiyar ga kasar ta Mali sannan za ta bukaci daukar matakin sanya takunkumi kan shugabannin soji da suka gudanar da juyin mulkin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!