Connect with us

Labarai

An fara babban taron koli na ECOWAS a Abuja

Published

on

Shugabannin kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ECOWAS sun hallara  a birnin Abuja don bude babban taron koli da za’a fara yau Lahadi.

Bayanai sun ce rashin tsaro da kuma juyin Mulki musamman masu sarkakiya da aka samu a Guinea Bissau da kuma yunkurinsa a jamhuriyar Benin za’a fi mayar da hankali a yayin wannnan ganawa ta musamman.

Taron na zuwa ne mako guda kacal bayan yunkurin juyin mulki da aka yi a Benin kan shugaban kasar Patrice Talon a kwatano, tare da rikicin siyasa a Guinea-Bissau da kuma tabarbarewar tsaro a arewacin kasashen gabar tekun yammacin Afirka.

Wannan shi ne taron koli na farko da Shugaban kasar Sierra Leone Julius Maada Bio ke jagoranta a matsayin shugaban ECOWAS, inda ake sa ran zai jagoranci yanke muhimman shawarwari kan tsaron yankin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!