Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

ilimi

An fara jin ra’ayoyin malamai kan samar da hukumar hana bara a Kano – Baba Impossible

Published

on

Gwamnatin Kano ta fara gayyato rukunin malamai a Kano domin tattaunawa tare da jin ra’ayin su kan samar da hukumar da za ta hana barace-barace a kan titi.

Kwamishinan ma’aikatar kula da addinai Muhammad Tahar Baba Impossible ne ya bayyana hakan a ranar Talata yayin ganawar sa da malaman.

“Gwamnatin ta  gayyaci  malaman ne don fahimtar da su  abinda hukumar za ta mayar da hankali akai idan aka samar da ita” in ji Baba Impossible.

Baba impossible ya kuma ce “Daga cikin waɗanda gwamnatin taji ra’ayoyin su akan samar da hukumar sun haɗa da masu kare haƙƙin ɗan Adam”.

Da dama daga cikin malaman da suka halarci tattaunawar sun nuna goyon bayan su kan samar da hukumar.

A makon da ya gabata ne gwamna Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana cewa, za a samar da hukumar da za ta hana barace-baracen almajirai akan titinan jihar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!