Connect with us

Ƙetare

An gano gawarwaki 270 bayan zaftarewar ƙasa Darfuf

Published

on

Wani jagoran farar hula a wani yanki na Darfur na kasar Sudan da ke ƙarƙashin ikon ‘yan tawaye ya ce an gano gawarwaki 270, bayan zaftarewar ƙasa da ta afka wa wani ƙauye da ke kan dutse.

 

Shugaban hukumar yankin, Mogeeb al-Rahman, ya ce ana kyautata zaton ɗaruruwan mutane maƙale a ƙarƙashin ɓaraguzan duwatsun.

 

Wani Bidiyo ya nuna yadda mazauna yankin ke haƙar ƙasa da hannayensu domin ceton rayuka.

 

A ranar Talatar da ta gabata ne, ƙungiyar ‘yan tawayen ta ce kusan duk mazauna ƙauyen waɗanda yawansu ya kai 1,000 sun mutu, in banda mutum guda kacal da ya tsira.

 

Sai dai rahotonni sun bayyana cewa, hukumomi ba su tabbatar da adadin mutanen da suka rasu ba kawo yanzu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!