Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Corona: An haramta wa matafiya daga kasashen Brazil, Indiya, Turkiya shigowa Najeriya

Published

on

Gwamnatin tarayya ta haramtawa matafiya daga kasashen India da Brazil da kuma Turkiyya shigowa Najeriya sakamakon tsananin da annobar cutar Corona ta yi a kasashen.

Shugaban kwamitin yaki da cutar na fadar shugaban kasa kuma sakataren gwamnatin tarayya Boss Mustapha ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar yau.

Boss Mustapha ya ce matakin zai fara aiki ne a ranar talata mai zuwa, sannan kuma za a sake nazartar batun bayan makonni hudu.

To sai dai ya ce ‘yan Najeriya mazauna wadannan kasashe da ke son shigowa kasar za a killace su har tsawon kwanaki bakwai domin tantance lafiyarsu kafin barin su su shigo cikin kasar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!