Labarai
An hallaka mutane 6 a sabbin hare-haren Filato

Mutane shida ne suka rasu a jihar Filato ciki har da mace guda a hare-hare daban-daban da suka auku a yankunan Bassa da Mangu.
Har ila yau, mutane goma sha biyu sun jikkata wadanda su ke kwance a asibiti suna samun kulawa.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa harin farko ya auku ne a kauyen Ancha da ke karamar hukumar Bassa, sai kuma wani hari na biyu a Gyenbwas Rinji da ke karamar hukumar Mangu.
Kafin haka kuma, wasu mutane hudu sun mutu, biyu kuma sun jikkata a wani hari a Uwok-Ishe, yayin da suke hanyarsu zuwa wuraren hakar ma’adinai.
Shugaban kungiyar Gan Allah Fulani (GAFDAN), Garba Abdullahi, ya ce mutanen da aka kashe a harin farko sun bace ne da misalin karfe 3 na dare yayin kiwon shanu. Daga bisani, aka tsinci gawawwakin su a kauyen Ancha.
You must be logged in to post a comment Login