Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

An kama wani matashi da kwalaben kodin 149- NDLEA

Published

on

Hukumar Hana sha da safarar miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta kama wani Mai suna Bashir Umar, dan shekaru Talatin da Biyar, Mazaunin Unguwar Hotoro Ladanai da kwalaben kodin Dari da Arbain da Tara da ake zargin yana safara da dilanci a yankin hotoro da sauran Unguwanni a nan Kano.

Shugaban hukumar ta NDLEA a nan Kano Abubakar Idris Ahmad ne ya bayana hakan, yayin zantawarsa da freedom rediyo a ranar Laraba.

Kwamandan hukumar wanda maimagana da yawun hukumar Sadiq Muhammad Mai Gatari yayi Magana a madadinsa, ya ce wannan Bashi ne karo na Farko da suka kama magidancin ba.

Mai Gatari, ya ce zasu fadada bincike akan matashin tare da daukar matakin da ya dace.

Ko da kuma zanta da matashin da ake zargi, yayi mana karin bayani kan yadda ya shiga hanun hukumar.

Hukumar Hana sha da safarar miyagun kwayoyin ta kuma gargadi masu safara ko dilancin miyagun kwayoyi da su tuba kafin fadawa komar hukumar, tare da yin Kira ga masu kishin kasa wajen sanar da Hukumar bayanan Sirri, Dan dakile sha da safarar miyagun kwayoyi a fadin jihar Kano da kasa baki daya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!