Connect with us

Kiwon Lafiya

An sake samun bullar cutar Corona a Najeriya

Published

on

Ma’aikatar lafiya ta jihar Cross River da ke kudu maso kudancin Najeriya ta tabbatar da samun mai ɗauke da cutar Corona a jihar.

Kwamishinan lafiya na jihar Dakta Henry Ayuk, wanda ya tabbatar da hakan ga manema labarai, ya ce an tabbatar da hakan ne a ranar 17 ga watan Afrilun 2026, kuma wani ɗan China da ya shigo ƙasar ranar 17 ga watan Maris ne ke ɗauke da cutar.

Ya ce jikin mara lafiyan ya yi tsanani ne a lokacin da ya ke wani asibiti da ke karkashin ofishin da ya ke aiki, kafin daga bisani aka garzaya da shi asibitin koyarwa na jami’ar Calabar.

A cewarsa bayan yi masa gwaje gwaje a asibitin ne aka tabbatar da cewa yana ɗauke da cutar, kuma a yanzu haka an killace shi.

Ya kuma buƙaci yan jihar da kar su tayar da hankalinsu, a cewarsa suna duk mai yiwuwa na hana cutar yaɗuwa, da ma duk wata cuta a jihar.

Hukumar hana yaduwar cututtuka ta Najeriya NCDC ta tabbatar da lamarin, kuma ta ce tana aiki da gwamnatin jihar domin shawo kan lamarin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!