Connect with us

Labaran Wasanni

An sallami Pele daga Asibiti

Published

on

Tsohon dan wasan kasar Brazil Pele ya koma gida bayan da aka sallameshi daga asibiti sakamakon jinya da ya sha.

Mai shekaru 80 ya kasance a bangaren masu kulawa ta musamman wato ICU tun a ranar 4 ga watan Satumbar daya gabata.

Mahukuntan asibitin ne dai suka sanar da sallamar Pele a wani rubutu da suka wallafa a shafin Internet a ranar Juma’a 01 ga watan Oktobar 2021.

Pele dan kasar Brazil wanda ya lashe gasar cin kofin Duniya har sau uku a shekarun 1958, 1962 da kuma 1970.

Kuma ya zama dan wasan guda da yafi kowa zura kwallo a tarihin kasar da yawan kwallaye 77 a wasanni 92 da ya buga.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!