Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ana gudanar da zaben cike gurbi a jihar Adamawa

Published

on

A yayin da aka fara gudanar da zaben cike gurbi a jihar Adamawa a yau, matainakin babban sifeton yan sandan kasar nan daga shiyya ta uku AIG Haruna Huzi Mrshalia ne ke jagorantar al’amuran tsaro a jihar.

 

Zaben dai zai gudana ne tsakanin yan takara biyu da suka hadar da gwamnan jihar Jibrila Bindow na jam’iyyar APC da kuma Ahmadu Fintiri na jam’iyyar PDP

 

Ko da yake a baya jam’iyyar APC ta yi barazanar kauracewa shiga zaben, sai dai a yammacin jiya ne kuma suka lashe aman su suka kuma amince da shiga zaben.

 

A yanzu haka dai an girke jami’an tsaro a ko ina a fadin jihar karkashin mataimakin sifeton yan sadan kasar Haruna Huzi domin tabbatar da tsaro yayin gudanar da zaben.

 

Hukumar zaben ta kasa INEC ce dai ta ayyana zaben jihar a matsayin wanda bai kammala ba bayan da aka samu tazarar kuri’u40, 988 inda aka samu matsaloli a rumfunan zaben 44 a cikn mazabu 28

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!