Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

ilimi

Ba jihar Bauchi ba ce ke da yawan yaran da basa zuwa makaranta ba -Ma’aikatar ilimi

Published

on

Ma’aikatar ilimin Najeriya ta ce labarin da ake yadawa a kafafen sada zumunta cewa jihar Bauchi ita ce ke kan gaba da adadin yaran da basa zuwa makaranta, ba gaskiya bane.

Sakataren yada labaran ma’aikatar Ben Goong, ne ya bayyana haka, yayin da yake zantawa da manema labarai jiya Juma’a a Abuja.

Marasa kishin kasa da son lalata harkar ilimi ne suka fitar da wata kalandar bogi – Ganduje

Goong, ya ce wadanda ke wallafawa labarin cewa yara miliyan 1 da dubu 239 da dari 759 ne ke gararamba akan titunan jihar Bauchi, suna yin hakan ne don zubar da kimar ma’aikatar ilimi.

Haka kuma ya bukaci daukacin al’umma da su yi watsi da irin wadandan labarai na karya a cewar sa ba su da fa’ida.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!