Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Dokar tsaftar muhalli a gobe bata shafi dalibai masu rubuta WAEC ba – Kabiru Getso

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta sahalewa Daliban dake rubuta Jarabawar kammala Sakandire ta yammacin Afrika WAEC fita a gobe asabar duk da cewa za a gudanar tsafatar muhalli a fadin jihar Kano.

Kwamishinan muhalli na jihar Kano Dakta Kabiru Ibrahim Getso ne ya bayyana hakan a yau lokacin da yake jawabi bayan kammala gudanar da duban tsaftar muhalli na kasuwanni da hukumomin gwamnati har ma tashoshin mota da ake gudanarwa a karshen kowanne wata.

Ya ce, ma’aikatar muhalli ta samar da wata shaidar da za a rabawa jami’an da ke sintirin raba kayan jarrabawar da kuma malaman da ke kula da rubuta jarrabawar ta yadda za su nuna a matsayin shaida a gobe don basu damar zuwa cibiyoyin rubuta jarrabawar.

Dakta Getso, ya kuma ce dalibai kuwa kayan makarantar su da kuma katin jarrabawar su zai zamo shaidar da za su fita a gobe asabar don rubuta jarrabawar.

Sai dai ya bukaci wadanda aka sahalewa dokar da su yi amfani da lokacin wajen isa guraren da wuri don baiwa jami’an tsaftar muhalli damar gudanar da ayyukan su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!