Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ba wanda aka bawa filin tashar rijiyar zaki-Gwamnatin Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta musanta batun cewa ta rabawa wasu mutane filaye a tashar mota ta Rijiyar Zaki, inda ta bukaci jama’a da su yi watsi da batun domin ba shi da tushe balle makama.

Mai Magana da yawun gwamnan Sunusi Bature Dawakin Tofa ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar aka rabawa manema labarai.

Sanarwar ta bayyana cewa ‘wasu marasa kishin Kano ne ke kokarin shafawa gwamnatin jihar kashin kaji domin kawar da hankalin jama’a daga irin nasarorin da aka samu kawo yanzu’.

A cewar Sunusi ‘masu wararen ne suka bukaci gwamnati ta sauya musu fasalin gurin domin guraren su bunkasa kuma su kara daraja a cikin birnin Kano’.

Rahoton: Abdulkadir Haladu Kiyawa

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!