Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

ba za mu lamunci amfani da kafofin yaɗa labarai don tayar da tarzoma a zaɓen 2023 ba – NBC

Published

on

Hukumar kula da kafafen yaɗa labarai ta ƙasa NBC ta ce, ba za ta lamunci yin amfani da kafofin yaɗa labarai don tayar da tarzoma a zaɓen 2023 ba.

Shugaban hukumar Alhaji Balarabe Shehu Ilela ne ya bayyana hakan a wata  ziyara da ya kai fadar gwamnatin Kano.

Ya ce, “A shirye muke don ganin yan siyasa ba su yi amfani da kafofin yaɗa labarai don cimma buƙatun su ba, ta hanyar tayar da tarzoma tsakanin al’umma”.

Alhaji Balarabe Ilela ya ce, haƙƙin masu kafafen yaɗa labarai ne na ganin sun hana yan siyasa yin amfani da kafafen don yin ɓatanci ga wasu.

“Dokokin hukumar mu sun hana bai wa kowa damar yin ɓatanci ga dan uwan su ko kuma yin kalaman da za su tayar da tarzoma”in ji Illela.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!