Connect with us

Labarai

Babbar kotun tarayya ta yi watsi da ƙarar PDP ɓangaren Turaki

Published

on

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yi watsi da ƙarar da wasu shugabannin jam’iyyar PDP suka shigar domin tilasta wa hukumar zaɓe ta INEC, ta amince da kwamitin riƙon ƙwarya na jam’iyyar ƙarƙashin jagorancin Kabiru Turaki.

Alƙali Salim Ibrahim ya yanke hukuncin cewa masu shigar da ƙarar ba su da hurumin gabatar da ƙarar. Saboda haka kotun ta ce ba ta da ikon sauraron shari’ar.

Alƙalin ya ce masu ƙarar sun kasa tabbatar wa kotu cewa INEC ta taɓa amincewa da kwamitin riƙon ƙwaryar da suke goyon baya, ko kuma cewa suna da ikon shigar da ƙara a madadin jam’iyyar PDP.

Shugaban kwamitin amintattu na PDP tsagin Turaki ƙarƙashin Sanata Adolphus Wabara, tare da wasu mambobin kwamitin ne suka garzaya kotu suna neman a umarci INEC ta sabunta bayananta tare da amincewa da kwamitin riƙon ƙwarya na jam’iyyar ƙarƙashin jagorancin Kabiru Turaki.

Sun kuma buƙaci kotun ta umarci hukumar zaɓen ta wallafa sunayen shugabannin riƙon ƙwaryar a shafinta na intanet.

Sai dai wani tsagin jam’iyyar ƙarƙashin jagorancin Abdulrahman Mohammed da ke samun goyon bayan ministan birnin tarayya, Nyesom Wike, ya nemi shiga shari’ar tare da ƙalubalantar ikon kotun, inda ya ce shi ne shugabancin PDP halastacce, kuma masu ƙarar ba su da hurumin shigar da ita a madadin jam’iyyar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!