Labarai
Iran ta kai hari a wuraren adana man Amurka

Sojojin Iran sun yi iƙirarin cewa sun kai hari kan wuraren ajiyar jiragen sama da tankunan adana man fetur a sansanin Sheikh Issa da ke Bahrain, wanda suka bayyana a matsayin sansanin Amurka, ta hanyar amfani da jiragen yaƙi marasa matuƙa.
A cikin sanarwar, sojojin sun kuma ce sun kai hare-hare kan gadoji da dama a Bahrain.
Sai dai kawo yanzu, hukumomin Bahrain ko na Amurka ba su fitar da wata sanarwa ba game da girman ɓarnar da aka yi, ko kuma ko akwai waɗanda suka jikkata ko suka mutu sakamakon hare-haren.
You must be logged in to post a comment Login