Connect with us

Kowane Gauta

Ban ce a fito da dan takarar shugabanci daga kudu ba – Ghali Umar Na’Abba

Published

on

Tsohon shugaban majalisar wakilan kasar nan Rt Hon Ghali Umar Na Abba ya musanta zargin da ake masa na marawa wani yanki baya na fito da dan takarar shugabancin kasa a shekarar 2023.

Hon Ghali Umar ya bayyana haka ne ta cikin shirin Kowane Gauta na gidan Radio Freedom, yana mai cewa ziyara ce kawai wata kungiya daga kudancin kasar nan suka kai masa domin neman shawararsa.

Yace maganar da yasan yayi da wadancen ‘yan kungiya ta matasa ya basu shawara ne cewa akwai mutane da suka can-canta a yankunansu musamman a cikin kabilinsu amma babu batun cewa a fito da dan takara daga yankin su.

Ghali Umar Na Abba ya kara da cewa gwamnatin yanzu ta gaza magance matsalolin da al’ummar Najeriya ke ciki wanda hakan yasa akabar mutane a cikin yinwa da fatara sakamakon gazawa da gwamnatin tayi a fili.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!