Labarai
Bangarorin siyasar Libya da ke takaddama sun sanya hannu kan yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya

Bangarorin siyasar Libya da ke takaddama sun rattaba hannu kan wata yarjejeniyar da Majalisar Dinkin Duniya ta goyi baya, wadda ake ganin za ta share fagen gudanar da zabukan kasa da aka dade ana jinkirta su.
An rattaba hannu kan yarjejeniyar ne a birnin Tripoli, a hedikwatar tawagar Majalisar Dinkin Duniya a Libya, yayin da shugabar tawagar, Hanna Tetteh, ta halarta.
Yarjejeniyar ta tanadi gudanar da zaben shugaban kasa da na majalisar dokoki cikin watanni 24, matukar an samu gwamnati guda da kuma dunkulewar hukumomin kasar.
Libya ta shafe shekaru tana fama da rikicin siyasa tun bayan hambarar da tsohon shugaban kasar, Muammar Gaddafi, a shekarar 2011.
A halin yanzu akwai gwamnatoci biyu da ke fafutukar iko da kasar, wato gwamnatin da Majalisar Dinkin Duniya ta amince da ita a Tripoli karkashin Firaminista Abdulhamid Dbeibah, da kuma wata gwamnati a gabashin kasar da ke samun goyon bayan kwamandan soji Khalifa Haftar.
You must be logged in to post a comment Login