Connect with us

Labarai

Sokoto: Yan Bindiga sun hallaka manoma 8 tare da raunata 5 a kauyen Ghandi

Published

on

Akalla manoma takwas ne aka kashe, yayin da wasu biyar suka jikkata sakamakon harin da wasu ‘yan bindiga suka kai a kauyen Ghandi da ke ƙaramar hukumar Rabah ta Jihar Sokoto.

Rahotanni sun ce maharan sun shiga yankin ne da misalin ƙarfe uku na ranar Lahadi, inda suka buɗe wa manoman wuta, lamarin da ya jefa mazauna yankin cikin fargaba.

 

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan Jihar Sokoto, DSP Ahmed Rufai, ya tabbatar da faruwar harin, yana mai cewa rundunar na tattara bayanai game da abin da ya faru.

Wani mazaunin yankin ya ce ana zargin harin da ɗaukar fansa ne, bayan da jami’an tsaro suka kashe wasu daga cikin ‘yan ƙungiyar ‘yan bindigar a yayin wasu samame da suka gudanar a yankin a kwanakin baya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!