Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Bidiyon Dala: Ganduje ya biya Ja’afar Ja’afar N800,000 saboda ɓata masa lokaci

Published

on

Gwamnan jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya biya ɗan jaridar nan Ja’afar Ja’afar Naira dubu ɗari takwas saboda ɓata masa lokaci.

A ranar Juma’ar nan ne Ja’afar Ja’afar ya shaida wa Freedom Radio cewa, Gwamnan ya biya shi dubu ɗari takwas kamar yadda kotu ta umarce shi.

A watan Yulin wannan shekara ne Babbar Kotun Kano mai lamba 9 da ke unguwar Bompai ƙarƙashin mai shari’a Sulaiman Baba Na Malam ta umarci Gwamnan ya biya Ja’afar Ja’afar da kanfaminsa kuɗin, saboda ɓata masa lokaci da yayi wajen shari’a.

An shafe shekaru huɗu ana fafata shari’a tsakanin Ja’afar da Gwamnan bayan da ya fitar da wasu faya-fayan bidiyo da ya nuna zargin Gwamnan da sunƙuma dalolin Amurka a aljihu.

Sai dai a watan Mayun wannan shekara ɗan jarida Ja’afar Ja’afar ya fice daga Najeriya zuwa birnin Landan.

Hakan ya biyo bayan zargin baraza da rayuwarsa da ya yiwa Gwamnatin Kano, bayan da Gwamna Ganduje ya musanta sahihancin bidiyon Dalar a wata hira da BBC Hausa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!