Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Bikin sabuwar shekara: Ba za mu amince da aikata baɗala ba a matsayin murna – Ibn Sina

Published

on

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta gargaɗi matasa da su guji wuce gona da iri a yayin bukukuwan sabuwar shekara.

Babban kwamandan hukumar Shiekh Harun Muhammad Sani Ibn Suna ne ya bayyana hakan a wani sauƙon murya da ya aikowa Freedom Radio.

Ibn Sina ya ce, suna sane da yadda matasa ke amfani da bukukuwan sabuwar shekara suna aikata baɗala da sunan murna.

“Haƙƙin iyaye ne ku san ina yaranku za su je, wane abu suke aikatawa da sunan murna, domin kuwa a shekarar bara mun ga yadda matasa suka riƙa baɗala da shaye shaye a ƙwaryar birni lamarin da ya sanya suka riƙa jikkata kan su” a cewar Ibn Sina.

“To mu Hisba ba za mu yarda da irin wannan ɗabi’u ba, don haka za mu baza jami’an mu lungu da sako don hanawa”.

Shiekh Harun Ibn Sina ya buƙaci iyaye su tsawatar da yaransu kan aikata munanan dabi’u.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!