Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Addini

Tahajjud: ba za mu yarda a fake da ibada a rika sabon Allah ba – Ibn Sina

Published

on

Hukumar Hisba ta jihar Kano ta gargadi matasa masu fita sallar Tahajjudi da su guji aikata ayyukan da ya sabawa ka’idojin addinin musulunci a yayin fita sallar.

Shugaban hukumar Sheikh Harun Mahammad Sani Ibn Sina ne ya sanar da hakan ta cikin wani sakon murya da ya aikowa Freedom Radio.

“Mun baza jam’an mu a dukkanin kananan hukumomi 44 na Kano, domin su sanya ido kan yadda ake karakainar zuwa sallar, don tabbatar da an bi dokoki”.

“Wasu bata gari na jan yan mata gefe su kafa dandalin hira yayin da suka fito sallar, to wannan dabi’ar ba za mu yarda da ita ba, kuma jami’an mu za su tabbatar ba samu masu yin ta ba” a cewar Ibn Sina.

Muhammad Harun Ibn Sina ya kuma ce, sun bai wa jami’an su umarnin su sanya ido kan ababen hawan masallata domin dakile ayyukan bata gari, kuma matukar aka kama wadanda suka karya doka to kuwa za su fuskanci hukunci.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!