Connect with us

Labarai

Boko Haram ta taɓa naɗa Buhari a matsayin mai shiga tsakani a tattaunawar sulhu- Jonathan

Published

on

Tsohon Shugaban ƙasa Goodluck Jonathan, ya bayyana cewa, ƴan ta’addar Boko Haram, sun taɓa naɗa tsohon Shugaban Najeriya marigayi Muhammadu Buhari a matsayin wakilinsu domin shiga tattaunawar sulhu da Gwamnatin Tarayya.

Jonathan ya bayyana haka ne a ranar Juma’a a Abuja, yayin kaddamar da littafin “Scars” da tsohon Hafsan Soja, Janar Lucky Irabor mai ritaya ya rubuta.

A cewar Jonathan, gwamnatinsa ta kafa kwamitoci daban-daban domin lalubo hanyar tattaunawa da ’yan Boko Haram, inda a wani lokaci cikin irin waɗannan shirye-shirye, mayakan suka ambaci Buhari a matsayin mutumin da suke son ya jagoranci tattaunawar.

Ya ƙara da cewa saboda haka, ya yi tunanin zai kasance da sauƙi ga Buhari lokacin da ya zama shugaban ƙasa ya tattauna da su har su mika wuya, amma lamarin yaƙin ya ci gaba da ɗaukar lokaci.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!