Connect with us

Labarai

Borno: Yan sanda sun fara kamen ababen hawa marasa lamba

Published

on

Rundunar ‘Yan sandan Jihar Borno ta fara kamen motoci da sauran ababen hawa da ba su da lamba da kuma wadanda ke rufe lambobinsu.

 

Jaridar Arewa Updates ta rawaito cewa, wannan na cikin sanarwar da Jami’in Hulda da Jama’a na Rundunar ‘Yan sandan Jihar, ASP Nahum Kenneth Daso, ya fitar a jiya Laraba.

 

Daso Ya ce, matakin na daga cikin kokarin dakile laifuka, inganta tattara bayanan sirri da kuma hana masu aikata laifuka amfani da motocin da ba su da sahihiyar rajista.

 

Sanarwar ta ce Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Borno, Naziru Abdulmajid, ya bukaci masu ababen hawa su tabbatar da cewa motocinsu suna da sahihiyar lambar rajista.

 

Rundunar ta yi gargadin cewa wadanda ke amfani da lambobin da aka rufe ko aka sauya za su fuskanci hukuncin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!