Labarai
Hukumar NCAA ta dakatar da lasisin kamfanin jirgin da ya sauka a titin mota

Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Kasa, wato NCAA, ta dakatar da lasisin kamfanin da ke gudanar da wani jirgin sama mai zaman kansa bayan da jirgin ya sauka a kan titin mota a yankin Ogwashi-Uku da ke kusa da Asaba a Jihar Delta.
Mai magana da yawun hukumar, Michael Achimugu, ya ce rahotannin farko sun nuna cewa jirgin ya kasa sauka yadda ya kamata a Filin Jirgin Sama na Asaba da misalin ƙarfe 7:43 na safiyar Laraba, lamarin da ya sa matukin jirgin ya sake yunƙurin sauka kafin daga bisani jirgin ya sauka a wani titi da ke yankin.
Sai dai hukumar ta tabbatar da cewa babu wanda ya rasa ransa ko ya samu munanan raunuka, domin duka fasinjojin da ma’aikatan jirgin sun fito lafiya daga cikin jirgin, sannan aka ɗauke su zuwa Asaba ta mota.
NCAA ta ce ta fara gudanar da bincike domin gano musabbabin aukuwar lamarin tare da ɗaukar matakan da suka dace.
You must be logged in to post a comment Login