Labarai
Kotun ta umarci INEC ta yi wa jam‘iyyar Access rajista

Kotun tarayya ta umurci hukumar zabe mai zaman kanta ta Najeriya INEC kan ta yi wa jam‘iyyar Access rajista.
Wata kotun tarayya wadda da ke zamanta a Abuja ce ta bayar da wannan umurnin, sannan ta umarci INEC ta ba jam’iyyar damar ƙarasa rajistarta.
Jagororin jam’iyyar Dr. Audu Bulama-Bukarti da Mevon Samuel su ne suka maka INEC a kotu, bayan hukumar zaben ta ƙi amincewa da ita, inda ta kafa hujja da cewa tambarin jam’iyyar ya yi kama da tambarin wata jam’iyyar.
Da yake yanke hukunci, alƙalin kotun Mai shari’a Obiora Atuegwu Egwuatu na kotu mai lamba 11, ya ce hukumar ba ta da hurumin hakan, inda ya nanata cewa hukuncin ba daidai ba ne, kuma ya saɓa da shari’a kamar yadda kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999 ya tsara da kuma sashe na 79 na kundin zaɓe na shekarar 2022.
You must be logged in to post a comment Login