Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Buhari zai yi titi daga Sokoto zuwa Nijar

Published

on

Gwamnatin tarayya ta amince da fitar da kudi naira biliyan ashirin da tara, na aikin kwangilar gina hanya daga Sokoto zuwa Jigawa ya zarce zuwa Jamhuriyyar Nijar.

Ministan ayyuka da gidaje, Babatunde Fashola ne ya sanar wa da manema labarai hakan jim kadan bayan kammala zaman majalisar zartarwa ta kasa wanda aka saba yi duk ranar Laraba da shugaba Muhammad Buhari, ke jagoranta a babban birnin tarayya Abuja.

Rahotanin sun bayyana cewar, a yayin zaman majalisar zartarwar an kwashe sama da awanni takwas ana gudanar da shi bisa jagorancin shugaban kasa da mataimakin sa Farfesa Yemi Osinbajo.

Labarai masu alaka:

APC zata daukaka kara kan shari’ar zaben gwamnan Sokoto

Ba muyi nadamar zabar Buhari ba -Izala

Babatunde Fashola, yace aikin za a faro shi ne daga yankin Belle da Kurdulla, dake ba kin  iyakar Najeriya da Jamhuriyar Nijar a bangaren na  jihar Sokoto.

Fashola, ya kara da ce wa kamfanin kwangila na hadin gwiwar wasu kamfanunuwa guda biyu ne, za su gudanar da aikin akan kudi fiye da naira biliyan ashirin da tara.

Haka kuma, aikin titin yana da nisan kilo mita 46 kuma ana saran cewar, za’a kammala shi cikin watanni 24, masu zuwa nan gaba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!