Connect with us

Labarai

CBN ya koka kan yadda ake wulakanta takardun Naira

Published

on

Babban Bankin kasa, CBN, ya koka kan yadda wasu daga cikin mutane ke wulakanta takardun kudi na Naira, ya na mai cewa hakan na kara tsadar buga sababbi da maye gurbin wadanda suka lalace.

 

Mataimakin Gwamnan Bankin, Dakta Bala Bello, wanda Daraktan Sashen Kula da harkokin Kudi da Rassa, Dakta Adedeji Adetona ya wakilta, ya bayyana haka a Abuja, yayin kaddamar da wani gangami na wayar da kan al’umma kan kula da takardun kudin naira.

 

Dakta Bello ya ce naira ba kawai takardar bace, illa alamar martabar kasa da ikon Najeriya, da  ya ce abubuwan da ake yi na sakaci kamar nadewa, yagawa, rubutu a kai, da yin watsi da su a lokutan bukukuwa na rage kimarta tare da kara tsadar kula da ita.

 

Ya yi gargadin cewa muddin ba a dauki matakan gyara ba, ‘yan kasa za su ci gaba da daukar nauyin kudin da ake buga sababbi domin maye gurbin wadanda aka lalata.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!