Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Coronavirus ta bulla a jihar Kogi

Published

on

Hukumar dakile yaduwar cutuka ta kasa NCDC tace an samu bullar cutar Covid-19 a jihar Kogi.

Cikin jadawalin wadanda suka kamu da cutar da NCDC ta fitar a ranar Laraba tace an samu mutane 2 dake dauke da cutar ta Coronavirus a jihar Kogi.

Kafin wannan rana dai jihar Kogi na cikin jihohi biyu a Najeriya da ba a samu bullar cutar ta Covid-19 ba, yanzu haka dai jihar Cross River ce kadai ba a samu bullar cutar ba a Najeriya.

A alkaluman da NCDC ta fitar a daren Laraba ta ce yazuwa yanzu mutane 8,733 ne suka kamu da cutar Covid-19 a sassa daban-daban na kasar nan.

Kuma 2,501 sun warke sarai har an sallame su.
Sai mutane 254 da cutar ta hallaka a Najeriya.

Hukumomi dai a kasarnan na cigaba da daukar matakan dakile yaduwar cutar a tsakanin al’umma.

A ranar Laraba ne gwamnatin tarayya ta amince ayi amfani da magungunan gargajiya wajen yaki da cutar ta Covid-19 a kasar nan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!