Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Covid-19: An saka “Lock Down” a kananan hukumomi 3 na jihar Bauchi

Published

on

Gwamnatin jihar Bauchi ta sanya dokar kulle da zaman gida ta tsawon kwana goma a kananan hukumomin Katagum, da Giade da karamar hukumar Zaki domin dakile yaduwar cutar Covid-19.

Gwamnan jihar Bauchi Sanata Bala Muhammad ne ya bayyana hakan a ranar Lahadi inda yace dokar zata fara aiki daga karfe 6 na yammacin ranar Talata.

Sanata Bala Muhammad yace, an dauki wannan mataki ne ganin yadda ake samun rahotonnin yaduwar cutar a yankin wadannan kananan hukumomi.

Kazalika gwamnan yace tuni kwamitin yakar Corona na jihar sun baza komarsu domin daukar dukkan matakan da ya dace wajen dakile cutar a yankunan.

A karshe gwamna ya bada umarni ga kwamitin rabon kayan tallafin Corona na jihar karkashin sarkin Bauchi Dakta Rilwanu Sulaiman Adamu da su kai agajin gaggawa ga al’umma a yankunan da dokar kullen zata fara aiki.

Karin labarai:

Da dumi-dumi Gwamnan jihar Bauchi ya kamu da COVID-19

COVID 19: Gwamnan jihar Bauchi ya killace kansa

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!