Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Yawan masu dauke da cutar HIV a Bauchi ya sauka – Gwamnati

Published

on

Gwamnatin jihar Bauchi ta ce adadin masu dauke da cuta mai karya garkuwar jiki a jihar ya sauka daga kaso 6, da ake dasu a tun daga shekarar 2001 zuwa sifili da digo 4 a shekarar 2019.

Kwamishinan lafiya na jihar Dr Aliyu Maigoro ne ya bayyana hakan, lokacin da yake jawabi ga me da matsayar jihar kan masu dauke da cutar, a wani bangare na bikin ranar yaki da cuta mai karya garkuwar jiki da aka gudanar a jiya.

Maigoro ya ce, a yanzu haka mutane dubu ashirin da biyar da dari takwas da tara ne ke rayuwa da cutar a kananan hukumomi 20 na jihar  Bauchi, cikin su kuwa mutum dubu ashirin da dari tara da sittin da daya suna samun kulawa daga cibiyoyin lafiya.

Cikin jawabin nasa, ya ce jihar za ta tabbatar da kowanne ma’aurata sun gudanar da gwaji kafin uare don dakile yaduwar cutar a tsakanin al’umma.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!