Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Covid-19: An sanya ranar komawa makarantu a Nijar

Published

on

Gwamnatin jamhuriyar Nijar ta bayyana ranar 1 ga watan Yuni mai zuwa a matsayin ranar da za’a sake bude makarantun bokon kasar bayan matakin rufe su na tsawon lokaci sakamakon bullar cutar Covid-19 a kasar.

Gwamnatin ta bayyana hakan ne ta bakin ministan ilimi mai zurfi na kasar Malan Yahuza Sadisu Madobi a yayin wani taron manema labarai da ya kira a babban birnin Yamai.

Ministan ya ce za a sake bude makarantun ne cikin matakan rigakafin cutar Coronavirus a cikin makarantun domin kammala shekarar karantun ta bana da ministan ya ce an ci sama da kashi 50 cikin 100 na karatun.

Labarai masu alaka:

Buhari zai yi titi daga Sokoto zuwa Nijar

Gwamnatin kasar Jamhuriyar Nijar ta ce zata yi aiki da kasarnan don bunkasa ilimi

Wakilin mu Yakuba Umaru Maigizawa ya waito mana cewa ministan ya kara da bayyana ranakun da za’a koma karatun na shekarar kamawa.

Sai dai bai bayyana ba ranar da za’a gudanar da jarabawar karshen karantun shekarar ta bana amma ya ce nan gaba gwamnatin za ta bayyana ranakun.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!