Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Covid-19: Gwamnati ta bada damar cigaba da sufuri a Nijar

Published

on

A dazu-dazun nan ne a yayin zaman majalisar ministoci da shugaba Isufu Mahamadu ya jagoranta gwamnatin Nijar ta bayyana matakinta na janye dokar hana jigila a fadin kasar baki daya.

Gwamnatin ta ce sakamakon cigaba da ake samu cikin yaki da cutar Covid-19 ne yasa ta dauki wannan mataki.

Wakilinmu Yakuba Umaru Maigizawa ya rawaito mana cewa baya ga wannan ma gwamnatin ta ce daga yanzu kofar babban birnin Yamai za ta kasance a bude bayan killace birnin na tsahon lokaci saboda Corona.

Dama dai al’umma na zaman jiran wannan mataki biyo bayan bude wuraren ibada da na sanar da ranar komawa makarantun boko a baya bayannan.

Tuni dai wasu manyan kamfanonin motocin masu sufiri a kasar da ma ketare suka fara fitar da sanarwar cigaba da ayyukansu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!