Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

COVID-19: Mun bankado matsalolin da bangaren kiwon lafiya ke fuskanta a Afrika – WAHO

Published

on

Kungiyar lafiya ta kasashen yammacin Afrika WAHO ta ce ta gano yadda cutar COVID-19 ta bankado matasalolin da bangaren kiwon lafiya ke da shi a asibitocin kasashen Afrika ta yamma.

Da yake ganawa da manema labarai  kan bikin cikar kungiyar shekaru 33 da kafuwa ta kafar Internet da kasashen Afrika goma sha biyar, shugaban kungiyar Farfesa Stanley Okolo ya ce gwamnatoci ba sa maida hankali wajen mangance matsalolin da al’umma ke fuskanta a asibitocin nahiyar Afrika.

Farfesa Stanley Okolo ya Ambato wasu daga cikin matsalolin da suka hada, rashin kayayyakin aiki da likitoci da dakunan gwaje-gwaje da magun-guna da na’urar gwada zafin jiki da kuma rashin alluran riga kafi.

Shugaban ya kara da cewar annobar Korona ta sanya an gano matasaloli masu tarin yawa da kuma hanyoyin da za’a bi wajen shawo kan su.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!