Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Covid -19:Kungiyar likitocin dabbobi ta bada tallafi

Published

on

Kungiyar likitocin dabbobi, ta kasa reshen jihar Kano, ta bada gudunmowar kayan wanke hannu a wani mataki na kokarin dakile yaduwar cutar Corona Virus, a fadin jiha da kasa baki daya.

Da yake jawabi lokacin mika tallafin  shugaban kungiyar likitocin dabbobi Dakta Abubakar Sani Inuwa,  ya ce sun bada  tallafin ne don agazawa  kokarin gwamnati na magance cutar covid 19 a jihar kano.

A nasa bangaren daraktan  hukumar kula da magunguna da bada su,  na jihar Kano kuma shugaban kwamitin karbar  tallafin magunguna na  cutar covid 19 da gwamnati ta kafa kan tallafawa al’umma, pharmacist  Hisham Imamuddeen,  ya bukaci mawadata su tallafawa marasa karfi  musamman ma a lokaci irin wannan.

Labarai masu alaka.

Covid-19: Ganduje zai fara raba tallafin kayan abinci

Covid 19- Fitilar Bichi ta raba kayan tallafi

Hisham Imamudden,  ya  bukaci hakan ne jim kadan bayan karbar tallafin da  kungiyar likitocin dabbobi suka  bayar na sinadarin wanke hannu ‘Hand Sanitizer’ guda dari biyar ga kwamitin domin rabawa al’umma mabukata.

Bilal Nasidi Mu’azu, wakilinmu da ya halarci taron rabon  yace  kungiyar ta  gudanar da feshin magani a gidan  namun daji dake nan kano tare da raba sinadarin wanke hannu  guda dari uku.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!