Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Manyan Labarai

CP Ahmed Iliyasu ya zama kwamishinan yan sandan Kano

Published

on

Babban sefeton ‘yan sanda na Najeriya Muhammadu Adamu ya bada umarnin da a gaggauta mayar da kwamishinan ‘yan sanda Ahmad Iliyasu zuwa jihar Kano a matsayin sabon kwamishina  bayan da wa’adin aiki na CP Wakili Mohammed ya kare.

A ranar 26 ga watan da muke ciki ne wa’adi aikin kwaminan ‘yan sanda Wakili Mohammed ya kare bayan ya kai shekaru 35 yana aiki.

Sabon kwamishinan ‘yan sandan na jihar Kano Ahmed Iliyasu na rike da digiri na 2 kan harkokin kasuwanci daga jam I’ar Ambrose Ali da ke Ekpoma kafin daga bisani a mayar da shi shalkwata rundunar ‘yan sanda dake Abuja, a matsayin babban jami’I.

Haka kuma a shekara ta 2016 zuwa watan Junairun wannan shekarar ya rike mukamin kwamishinan ‘yan sanda na jihar Ogun.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!