Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Cutar Maleriya ta hallaka mutane dubu dari shida da goma sha tara a Najeriya – WHO

Published

on

Hukumar lafiya ta duniya WHO ta ce kashi 31 cikin dari na mutanen da zazzabin cizon sauro wato maleriya ya hallaka a duniya a bara yan Najeria ne.

Wannan na cikin rahotan maleriya da hukumar ta fitar tana mai jadda cewa duk da tasirin cutar Covid 19, da ake ci gaba da gani a halin yanzu zazzabin cizon sauran na ci gaba da halaka mutane a duniya.

WHO ta ce cutar ta hallaka mutane dubu dari shida da goma sha tara a bara bayan da ta kama mutane miliyan dari biyu da arba’in da bakwai adadin da ya zarce na shekarar 2019.

Shugaban hukumar ta WHO Tedros Adhanon Ghebreyesus ya bukaci kasashen duniya da su tashi tsaye tare da kara kaimi wajen yakar cutar zazzabin cizon sauran, dan kare rayukan al’ummar su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!