Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

WHO ta amince a fara amfani da rigakafin allurar zazzabin Maleria

Published

on

Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta amince da fara amfani da nau’in allurar rigakafin zazzabin cizon sauro na Malaria, nau’in allurar da ke matsayin irinsa na farko da hukumar ta amince da amfani da shi kan jama’a don yaki da cutar.

A jiya Laraba 06 ga watan Oktobar 2021 ne WHO ta amince da rigakafin da wani kamfani mai suna GlaxoSmithKline ya samar.

Cutar zazzabin cizon sauro ta Malaria dai na kashe akalla mutanae Miliyon 500 a duk shekara a yankin Afrika kadai da mafi akasarin su yara ne kanana.

Matakin na WHO na zuwa bayan gwajin alluran rigakafin na Malaria ko kuma zazzabin cizon sauro har fiye da miliyan 2 a kasashen Ghana Kenya da kuma Malawi cikin shekarar 2019.

Sanarwar da WHO ta fitar ta ruwaito Pedro Alonso daraktan shirin yaki da Malaria na hukumar na cewa matakin babban ci gaba ne a yaki da cutar da kan kashe yaro guda duk bayan mintuna biyu.

Cutar ta Malaria da sauro ke yadawa na jerin cutuka mafiya kisa yanzu haka a Duniya, inda tafi kamari a kasashen Afrika da gabashin nahiyar Asiya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!