Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Da dumi-dumi : Tsohun gwamnan jihar Kaduna ya rasu

Published

on

Allah yayiwa Gwamnan tsohuwar jihar Kaduna kuma shugaban jam’iyyar PRP na kasa Alhaji Abdulkadir Balarabe Musa rasuwa da safiyar yau.

Iyalan marigayi tsohon gwamnan tsohuwar jihar Kaduna sun bayyana cewa, za a gudanar da sallar jana’izar marigayin da misalin karfe hudu na yamma.

yar marigayin Zulai Balarabe Musa ce ta bayyanawa freedom Rediyo hakan, tana mai cewa ana sa ran Dakta Gumi ne zai sallaci gawar tasa.

‘Yar marigayin wacce tsohuwar mai kula da sashen yada labarai ta hukumar kula da kafafan yada labarai na jihar Kaduna ce Hajiya Zulai Balarabe Musa.

Zulai Balarabe Musa ta bayyana cewa marigayin da ya sha fama da rashin lafiya, kafin rasuwar sa

Tana mai cewa Maihaifin nasu ya rasu ya bar Mahaifiyar su da ‘ya’ya takwas da kuma jikoki da dama.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!